Ƙungiyar marubuta kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya HURIWA, ta zargi ƙasashen Rasha da Isra'ila da neman fin ƙarfin Majalisar Ɗinkin Duniya.
A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ce an wayi gari da mutuwar ƴanjarida guda huɗu a sanadiyar wani hari da Isra'ila ta kai a wani asibitin Gaza, bayan ƴanjarida biyar da aka kashe a kwanakin baya.
Ƙungiyar ta ce wani rahoton sirri na sojojin Isra'ila ya nuna cewa yawancin waɗanda aka kashe a Gaza fararen hula ne.
Sanarwar ta ce alƙaluman da binciken haɗin gwiwa da kafofin watsa labarai na The Guardian da Mujallar +972 da Local Call suka gudanar ya gano cewa, "zuwa watan Mayun 2025, kimanin wata 19 da fara yaƙin Isra'ila a Gaza, sojojin Isra'ila sun daddale mayaƙan Hamas 8,900 da na PIJ da ko dai suka tabbatar da mutuwarsu, ko kuma suke tunanin sun mutu, sannan ma'aikatar lafiyar zirin ta ce aƙalla mutum 53,000 ne suka mutu."
HURIWA ta ce hakan ke nufin cewa kashi 17 ne kawai na waɗanda aka kashe ne mayaƙa, sannan sauran kashi 83 fararen hula ne.
Haka kuma ta ce tun bayan fara yaƙin Rasha a Ukraine, dubban ƴan ƙasar Ukraine, waɗanda HURIWA ta ce fararen hula sun fi yawa.
"Yadda Rasha da Isra'ila ke kai hari kan ƙananan ƙasashe irin su Ukraine da Falasɗinawa, da yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ke zama tarukan majalisar tsaro, ta fitar da sanarwa da matakai amma ba sa haifar da ɗa mai ido ya nuna akwai lauje cikin naɗi. Kasancewar Rasha na da kujerar na-ƙi, sannan Isra'ila na samun goyon bayan Amurka wadda ita ma take da kujerar na-ƙi, hakan ya sa Rasha da Isra'ila ba sa jin ɗarɗar kan barazanar da Majalisar Ɗinkin Duniya ke musu na karya dokokin duniya."