Sojojin Chadi sun kashe mayaƙan Boko Haram aƙalla 300 a yammacin ƙasar
Sojojin Chadi sun ce sun kawo ƙarshen yaƙin da suka shafe watanni huɗu su na yi da mayaƙan Boko Haram a yammacin ƙasar.
Sojojin sun ce sun kashe aƙalla masu iƙirarin jihadi 300, kuma a yanzu ƙungiyar ba za ta sake yin tasiri a yankin ba.
Shugaba Mahamat Idris Deby Itno ne ya ƙaddamar da hare-haren a watan Oktoban da ya gabata bayan gagarumin harin da Boko Haram ta ka wa sansanin soji a yankin tafkin Chadi.
Ƙungiyar Boko Haram ta fara ayyukan ta'adanci ne a Najeriya a shekarar 2009 wanda tuni ya bazu zuwa ƙasashe makwabta.