Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na Laraba 12/11/2025.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Muhammad Annur, Badamasi Abdulƙadir

  1. Majalisar Dokokin Najeriya ta amince Tinubu ya ciwo wani sabon bashi

    Majalisar Dokokin Najeriya ta amince wa shugaban ƙasar Bola Tinubu ya ci wani ƙarin bashi a cikin gida na naira tiriliyan 1.15 domin cike giɓin da ke cikin kasafin kuɗin 2025.

    Makonni biyu da suka gabata ne shugaban ƙasar Bola Tinubu ya buƙaci majalisar ta amince da ciyo bashin, inda ya kafa hujja da ƙarin da aka samu a giɓin kasafin kuɗin ƙasar daga naira tiriliyan 12.95 da ya gabatar, zuwa naira tiriliyan 14.10 da majalisar dokokin ta amince da shi.

    Kasafin kuɗin Najeriya na 2025 ya kai jimillar kudi naira tiriliyan 59.99, inda ake sa ran cike giɓin ta hanyar cin bashi a ciki da kuma wajen ƙasar.

    A makon da ya gabata ƙasar ta samu kuɗi dala biliyan 2.35 ta hanyar takardun lamuni na Eurobond.

  2. Najeriya na cikin ƙasashen da tarin TB ya fi kashe mutane

    Hukumar lafiya ta duniya ta ce tarin TB na ci gaba da zama cutar da ke kan gaba wajen kashe mutane a duniya, inda a bara kaɗai ta kashe mutane miliyan ɗaya da dubu ɗari uku.

    Hukumar ta yi gargaɗin cewa ana samun koma baya a nasarar yaƙi da cutar.

    Yawan mutane da cutar ke kashewa ya ragu da kashi uku daga ƙididdigar 2023, kuma an samu raguwar masu kamuwa da cutar da aƙalla kashi biyu.

    Mutane aƙalla miliyan goma da dubu ɗari bakwai suka kamu da tarin TB a 2024, kuma ƙididdiga ta nuna cewa miliyan biyar da dubu ɗari takwas maza ne yayin da miliyan uku da dubu ɗari bakwai mata ne. Sai kuma ƙananan yara miliyan ɗaya da dubu ɗari biyu.

    Cutar wadda ake iya rigakafin ta, tana yaɗuwa ta iska daga tarin mai ɗauke da ƙwayoyin ta, kuma tana shafar huhun mutum ne kai tsaye.

    Hukumar lafiya ta duniya ta ce a bara, an samu mafi yawan masu kamuwa da sutar ne a ƙasashe takwas da suka haɗa da India (kashi 25) da Indonesia (kashi 10) da Philippines (kashi 6.8) da China ( kashi 6.5) da Pakistan (kashi 6.3) da Najeriya (Kashi 4.8) da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo (Kashi 3.9) da kuma Bangladesh (kashi 3.6).

  3. Mutane shida sun mutu wajen neman shiga aikin soja a Ghana

    Mutane aƙalla shida sun mutu yayin da wasu 22 suka sami rauni a wani hatsari a wajen ɗaukar aikin soji a Ghana.

    Rundunar sojin ta ce matasa masu neman aiki ne suka ture shingen jami'an tsaro kuma suka yi tururuwa cikin filin wasa na birnin Accra, inda aka samu asarar rayuka.

    Rashin aikin yi a ƙasar Ghana mai ɗimbin matasa ya kai kashi 32 cikin ɗari, lamarin da janyo cunkoso a cibiyoyin ɗaukar aiki.

    Shugaban Ghana, John Mahama, ya ce gwamnatinsa ta ƙudiri aniyar bai wa dukkan matasan ƙasar damar shiga aikin soja.

    Hukumomi sun ci gaba da aikin tantance masu neman shiga sojan bayan ƙura ta lafa, inda suka bayar da tabbacin ɗaukar matakan kariya.

  4. MDD ta nuna damuwa kan ƙangin yunwa a Najeriya

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa za a samu ƙarin miliyoyin mutane da ke fuskantar barazanar yunwa a wauraren da ake fama da rikici a sassan duniya.

    Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya biyu ne suka fitar da gargaɗin a ranar Laraba, inda suka ce wuraren da abin zai shafa sun haɗa da Sudan da kuma Gaza, tare da yin kiran samar da kuɗaɗe domin cike gurbin da aka samu bayan rage tallafin ƙasashen duniya.

    A wata sanarwar haɗin gwiwa, shirin samar da abinci na duniya da hukumar samar da abinci da bunƙasa aikin noma ta Majalisar Dinkin Duniya sun lissafa sauran ƙasashen da ke fuskantar baraznar da suka haɗa da Haiti da Mali da Sudan ta Kudu da kuma Yemen, inda suka ce za a yi fama da matsananciyar yunwa.

    Akwai kuma wasu ƙasashen da aka yi gargaɗin za su fuskanci matsalar yunwa amma ba kamar jerin ƙasashen farko ba, kuma sun haɗa da Afghanistan da jamhuriyar dimokuradiyyar Congo da Myanmar da Najeriya da Somalia da kuma Syria.

    Hukumomin sun ce akwai buƙatar ƙara samun masu bayar da tallafi a tsakanin gwamnatoci da kuma ƙungiyoyi, domin a cewar su a ƙarshen watan Oktoba tallafin dala biliyan goma da rabi suka samu daga cikin dala biliyan 29 da aka yi kasafi domin tanadin tallafin yaƙi da yunwa.

    Amurka ce ta fi bayar da tallafi mai yawa ga Majalisar Dinkin Duniya a bara, amma a bana ta rage yawan tallafin da take bai wa ƙasashen waje, kuma akwai wasu ƙasashen da suka rage tallafin da suke bayarwa.

  5. Mu na bincike kan rikicin Wike da sojoji - Badaru

    Ministan tsaron Najeriya Mohammed Badaru, ya ce ma'aikatarsa na bincke a kan jayayyar da aka samu tsakanin ministan birnin tarayyar ƙasar, Abuja Nyesom Wike da kuma wani hafsan sojin ruwa, A. M. Yerima a kan dambarwar ikon mallakar fili.

    A yayin wani taron manema labarai a Abuja, Badaru ya ce rundunar sojin Najeriya ba za ta taɓa juya baya ga duk wani jami'inta da ke gudanar da aikinsa a kan doka ba.

    Badaru ya sanar da hakan ne bayan jayayyar da aka yi tsakanin Nyesom Wike da jami'in sojin ruwa, A.M Yerima a ranar Talata 11 ga watan Nuwamba, lamarin da ke ci gaba da jan hankalin jama'a a ƙasar.

    Ministan ya ce "A matsayin ma'aikata da kuma rundunar sojin Najeriya, za mu kasance masu bayar da kariya ga duk wani jami'inmu da ke kan ƙa'idar aikinsa.

    "Muna nazari kan batun, kuma muna bayar da tabbacin cewa za mu kare duk wani jami'inmu da ke kan aikinsa bisa doka. Ba za mu taɓa bari wani abu ya faru da jami'inmu da kje gudanar da aikinsa yadda doka ta yi tanadi ba.''

    A ranar Talata bidiyon jayayya tsakanin ministan birnin Abuja da wani matashin hafsan sojin ruwa ya karaɗe kafafen sada zumunta, inda ministan ya yi jayayya da sojan a kan wani fili da ake ginawa mallakin tsohon babban hafsan sojan ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo.

    Wike da tawagrasa sun ziyarci wajen da filin yake tare da neman a nuna masu takardun izinin mallakar filin.

    Ministan ya haƙiƙance cewa ba a cika ƙa'ida ba wajen mallakar takardun filin.

    Sojojin kuma sun hana ministan shiga filin, lamarin da ya fusata shi har ta kai ga musayar kalamai.

  6. An gano motar ofishin mataimakin gwamnan Kano da aka sace

    'Yansanda sun yi nasarar gano motar tawagar ofishin gwamnan jihar Kano, ƙirar Toyota Hilux da aka sace kwanan nan, tare kuma da kama wanda ake zargi da satar

    Wata sanarwa da ofishin mataimakin gwamnan ya fitar, wadda ta tabbatar da hakan ta ce a rahoton da suka samu daga 'yansanda sun tabbatar musu cewa sun gano motar ne da sanyin safiyar Larabar nan, sakamakon aikin haɗin gwiwa na gaggawa na jami'an tsaro.

    Sanarwar ta ce an kama wanda ake zargi da satar wanda cikakke ma'aikaci ne - direba na gwamnati, kuma yana taimaka wa wajen gudanar da binciken da ake yi kan lamarin.

    Ofishin mataimakin gwamnan ya bayyana satar da cewa cin mana ce ƙarara da direban ya yi.

  7. Isra'ila ta ce ta sake buɗe mashigar Zikim don shigar da kayan agaji Gaza

    Isra'ila ta ce ta sake buɗe muhimmiyar mashigar nan ta Zikim da ke arewacin Gaza domin bari a shigar da kayyayakin agaji yankin.

    A wata sanarwa da rundunar sojin Isra'ila ta fitar, ta ce a yanzu za a iya shigar da kayyayaki cikin manyan motoci, bayan jami'an tsaron Isra'ila sun gudanar da bincike.

    Kungiyoyin agaji na Majalisar Ɗinkin Duniya sun sha kiran a buɗe mashigar domin bayar da damar shigar da agaji zuwa arewacin Gaza da ke fama da yunwa.

    Sun ce an rufe mashigar ne tun a watan Satumba kuma babu wani abu da ya shiga tun lokacin. Akasarin kayayyakin tallafin da su ka shiga Gaza, sun shiga ne ta mashigar Karem Shalom da ke kudanci.

  8. Pakistan na barazanar kai wa Afghanistan hari bayan fashewar bam a Islamabad

    Ministan tsaron Pakistan ya ce ƙasarsa ba za ta kawar da yiwuwar ɗaukar mataki kan Afghanistan ba, bayan fashewar wani bam a wajen ginin wata kotu a babban birnin ƙasar, Islamabad.

    Khawaja Muhammad Asif, ya ce irin waɗannan hare-haren na iya kasancewa mafarin kai wa ƙasar hare-hare nan gaba daga Afghanistan.

    Alaka tsakanin ƙasashen biyu na ƙara taɓarɓarewa a 'yan watannin da suka gabata.

    Pakistan na zargin 'yan Taliban na Afghanistan da bai wa ƙungiyoyin 'yanbindiga mafaka, inda ta ke zargin ana kitsa hare-haren da ake kai mata a cikin iyakokin Afghanistan.

    Gwamnatin Taliban ta musanta wannan zargin.

  9. Trump ya nemi shugaban Isra'ila ya yi wa Netanyahu afuwa kan shari'ar rashawa

    Donald Trump ya aike wa shugaban Isra'ila wasika, yana bukatarsa ya yi wa Firaministan Isra'ila afuwa kan zargin aikata laifukan cin hanci da rashawa.

    Ofishin Shugaba Isaac Herzog ya ce wasikar ta bayyana shari'ar da ake yi da Mista Netanyahu a matsayin wani abu na siyasa kuma wanda bai dace ba.

    Mista Herzog ya mayar da martani, inda ya ce yana ganin mutuncin Shugaba Trump sosai, amma duk wanda yake so a yi wa Netanyahu afuwa sai ya gabatar da bukatarsa bisa sharuddan da aka gindaya.

    Mista Netanyahu ya musanta aikata cin hanci, da yaudara da cin amana, laifukan da ake tuhumarsa da aikatawa kuma ake shari'ah kansu tun shekarar 2020.

  10. An kwaso ƙarin 'yan Najeriya 180 da suka maƙale a Libya

    Hukumomin Najeriya sun karɓi 'yan ƙasar 180 waɗanda suka siffanta da "marasa galihu da suka maƙale a Libya" bayan kwaso su ranar Talata.

    Hukumar bayar da agaji ta ƙasa National Emergency Management Agency (Nema) ta ce mutanen sun sauka a filin jirgi na Murtala Muhammed da ke Legas.

    Daga cikinsu, akwai maza manya 45, da mata manya 102, da yara maza shida, da kuma yara mata 13. Haka nan, akwai jarirai maza da mata bakwai-bakwai.

    Sanarwar ta ƙara da cewa 46 daga cikin 'yan Najeriyar da aka kwaso ba su da lafiya, abin da ya sa aka wuce da su wurin kula da lafiyarsu.

    Ƙungiyar kula da harkokin 'yan gudun hijira ta duniya International Organization for Migration (IOM) ce ta ɗauki nauyin jiglar bisa haɗin gwiwa da hukumomin Najeriya.

  11. Ina sane na yi calikanci a bidiyon da na yi a London - Doguwa

    Shugaban masu rinjaye na majalisar Wakilan Najeriya, Hon Alhassan Doguwa ya shaida wa BBC cewa kaikomo tare da yin ƙwambo da aka ga yana yi a cikin wasu bidiyoyin da suka bayyana a soshiyal midiya, ya yi su ne domin aikewa da saƙo ga abokan hamayyarsa na siyasa.

  12. 'Yansandan Kebbi sun ceto mutane bayan kashe ɗanfashi

    Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kebbi ta ce ta kashe ɗanfashi ɗaya cikin takwas da suka shiga gidan wani mutum a ƙaramar hukumar Maiyama.

    Wata sanarwa da kakakin rundunar CSP Nafiu Abdullahi ya fitar ta ce an sace mutum biyu, Muhafi Sani da Shamsiya Aliyu, yayin harin da 'yanbindigar suka kai ranar Talata.

    CSP Nafiu ya ce bayan sun samu rahoton faruwar lamarin ne suka bi sawun maharan ƙarƙshin jagorancin DPO na Maiyama a tawagar da ta ƙunshi 'yansanda da 'yan sa-kai.

    "Sakamakon haka aka kashe ɗaya daga cikin 'yanfashin tare da ƙwace bindigarsa harba-ruga da kuma ƙunshin harsashi ɗaya," in ji shi.

    Ta ƙara da cewa wasu 'yanbindigar sun far wa garin Giron Masa na ƙaramar hukumar Shanga, inda suka sace mutum biyu nan ma.

    "Yayin fafatawa da 'yanbindigar, masu garkuwar sun gudu cikin daji da raunuka kuma suka bar mutanen da suka kama."

  13. Kotu ta ɗaure ɗan tsohon shugaban Gabon da mahaifiyarsa shekara 20

    Wata kotu a Gabon ta yanke wa ɗan hamɓararren shugaban kasar Ali Bongo da kuma uwargidansa ɗaurin shekara 20 a gidan yari bayan shari'ar kwana biyu.

    Noureddin Bongo da Sylvia Bongo – waɗanda aka yi wa shari’ar a bayan idonsu – an same su da laifin almubazzaranci da kuma karin wasu laifuka.

    Sun kasance masu tafiyar da gwamnati a Gabon sakamakon mutuwar ɓarin jiki da Ali Bongo ya samu a 2018 kafin a hamɓarar da gwamnatinsa a juyin mulki.

    An kama matar da ɗanta ne bayan juyin mulkin, aka tsare su na tsawon wata 20 kafin aka sake su a watan Mayu kuma aka ba su damar barin ƙasar.

  14. Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba - Ministan Abuja Wike

    Ministan Abuja babban birnin Najeriya, Nyesom Wike, ya ci alwashin hana yin gini a duk wani fili da aka mallaka ba bisa doka ba bayan arangamar da ya yi da sojoji ranar Talata.

    Kalaman nasa na zuwa ne jim kaɗan bayan wasu dakaru sojan ruwa na Najeriya sun hana ministan da tawagarsa shiga wani fili da ke unguwar Gaduwa a birnin na Abuja.

    Bidiyo da hotunan hatsaniyar tasu sun karaɗe shafuka sada zumunta a Najeriya, inda aka ga ministan yana ta cacar baki da jagoran sojojin wanda ya ce maigidansa ya ba shi umarnin hana kowa shiga.

    "Na ba su [jami'an FCTA] umarnin su tabbatar ba a yi wani gini matuƙar ba su da takardun izini ko na mallaka," kamar yadda Wike ya faɗa wa manema labarai a wurin hatsaniyar.

    Ministan ya zargi sojojin da mallakar fili ba bisa ƙa'ida ba, inda koka game da amfani da dakaru wajen bai wa filaye kariya.

  15. Dalilin da ya sa na rinƙa ƙwambo a bidiyoyina a London - Ado Doguwa

    Shugaban masu rinjaye na majalisar Wakilan Najeriya, Hon Alhassan Doguwa ya shaida wa BBC cewa kaikomo tare da yin ƙwambo da aka ga yana yi a cikin wasu bidiyoyin da suka bayyana a soshiyal midiya, ya yi su ne domin aikewa da saƙo ga abokan hamayyarsa na siyasa.

    A wata tattaunawa da ya yi da BBC a birnin Landan, Alhassan Doguwa ya ce

    "Na zo Landan a daidai wata gaɓa da nake son na aika wa ƴan siyasa wani saƙo musamman maƙiyanmu da suka mayar da siyasa ta koma gaba da ƙiyayya. Musamman ƴansiyasarmu na Doguwa da Tudunwada waɗanda ke siyasa idanunsu a rufe."

    Saboda haka na zo Ingila ina yin waɗannan hotunan ne domin na yi walwala na wataya nuna wa ƴan jihar Kano maƙiyana da waɗanda suka fito daga Doguwa da Tudun Wada maƙiyana cewa gani dai ni ne dai wakilin Doguwa da Tudun Wada da an ƙi da an so Allah ya yarda, kuma ga ni a Ingila, to abu ne nake yin shi kamar wani cali-cali kuma saƙon ya je" in ji Doguwa.

    Ɗan majalisar ya kuma yi ƙarin haske dangane da dalilin da ya sa ya rinƙa ƙwambo a cikin bidiyoyin.

  16. Hazo ya taimaka wa dakarun Rasha ƙwace ƙarin yankuna a Ukraine

    Hazo ya taimaka wa dakarun Rasha kutsawa cikin garin Pokrovsk da ke gabashin Ukraine.

    Bataliyar 7th Airborne Assault Corps ta dakarun Ukraine ta ce yanayin ya sa dakarun Rasha sun tsananta yunƙurin ƙara nausawa cikin birnin da zimmar yi wa sojan Ukraine ƙawanya.

    Dakarun Rasha sun shafe fiye da shekara ɗaya suna ƙoƙarin ƙwace birnin. Yanzu Ukraine ta ce akwai yiwuwar dakarun Rasha 300 zuwa 500 sun shiga yankin kuma Shugaban Ukraine Zelensky ya ce lamarin "ya yi ƙamari".

    A gefe guda kuma, hafsan sojan ƙasa na Ukraine Oleksandr Syrskyi ya ce halin da dakarunsa ke ciki kudu maso gabashin Zaporizhzhia "ya tsananta sosai" bayan an ƙwace ƙauyuka uku daga hannunsu.

  17. Shirye-shiryen gwamnatin Najeriya ba su rage talauci ba - Bankin Duniya

    Bankin Dunya ya ce kuɗaɗen kasafin da gwamnatin Najeriya ke kashewa kan shirin walwalar jama'a bai kai yawan na sauran ƙasashen hamadfar Afirka ba kuma bai yi wani tasiri wajen talauci ba a ƙasar.

    Cikin wani sabon rahoto, bankin ya ce kasafi na 0.14 cikin 100 na arzikin cikin gida na Najeriya bai kai 1.1 ba da sauran ƙasashen Afirka suka saba warewa duk shekara domin inganta rayuwar 'yan ƙasarsu.

    Rahoton wanda ya duba dukkan shirye-shiryen da gwamnatin Najeriya ke aiwatarwa, ya nuna cewa talauci ya ragu ne da maki 0.4 kacal a Najeriya.

    Kasafin ya yi ƙasa sosai, inda wasu bayanai daga cibiyar ƙwadago ta duniya ILO suka nuna bai wuce kashi 0.45 ba duk shekara tun daga 2010 zuwa 2021.

    Duk da cewa akwai alƙaluma daban-daban, bayanai a 2019 sun nuna kasafin a kan kashi 0.7 cikin 100 na arzikin cikin gida idan aka cire ɓangaren lafiya.

  18. Trump ya haƙikance zai maka BBC a kotu

    Shugaban Amurka Donald Trump ya sake nanata aniyarsa ta maka BBC a kotu a kan wani fim game da abubuwan da suka faru na tarzomar ginin majalisar Amurkar a 2021.

    Mista Trump ya ce ya kamata ya yi hakan tare da zargin BBC da yaudarar jama'a.

    Tun da farko ya yi barazanar shigar da BBC ƙara tare da neman diyyar dala biliyan ɗaya.

    Tuni babban daraktan BBC da kuma shugabar sashen labarai suka yi murabus bayan tabbatar da sauya wasu bangarori biyu na jawabin Mista Trump, wanda ya nuna ya karfafa tarzomar da magoya bayansa suka haddasa a ranar 6 ga watan Janairu.

  19. Barkanmu da hantsin Laraba

    Maraba da shigowa shafin labarai kai-tsaye, wanda zai kawo rahotonni daga sassan duniya.

    NI ne Umar MIkail zan kasance da ku daga yanzu har zuwa ƙarfe 4:00 na rana.

    Ku biyo mu.