Wata majiya mai
karfi daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon-kasa, ta EFCC ta tabbatar wa BBC cewa hukumar na ci gaba da tsare, shugaban hukumar alhazan Najeriya, Jalal Arabi tare da sakataren hukumar Abdullahi Kontagora.
Ana zargin shugaban da yin sama da fadi da wani bangare na naira biliyan 90 da gwamnatin Najeriya
ta ba hukumar a matsayin tallafi ga aikin hajjin 2024 da ya gabata.
Hukumar ta ce an gano kudin da
yawansu ya zarta Riyal dubu 300 daga hannun shugaban da
wasu manyan jami’an hukumar hajjin ta Najeriya.
EFCC ta kara da cewa bincikenta ya gano shugaban hukumar ya yi amfani da wani bangare na naira
biliyan 90 din da gwamnatin Najeriya ta bai wa hukumar aikin hajjin a
matsayin kudaden tallafi wajen biyan kansa da manyan jami’an kudaden da suka
wuce kima.
Bayanan sun nuna
cewa hukumar na neman bahasi ne game da yadda aka kashe naira biliyan 90 da
gwamnatin tarayya ta bai wa NAHCON a matsayin tallafi ga mahajjatan Najeriya na 2024 da aka kammala a watan Yuli.
Kazalika,
hukumar EFFCn ta ce a kasafin kudi na bana ainihin kudaden da aka warewa
kwamishinoni da manyan daraktoci da ma’aikatan hukumar sun saba yadda suka
tsara nasu tare da wawure kaso mafi yawa daga abin da aka kayyade ma kowanensu.
Majiyar ta EFCC
ta kara da cewa ana zargin shugaban hukumar hajjin da ware wa kansa Riyal dubu
hamsin a maimakon riyal dubu goma sha biyar da dari tara da shirin da tara da
aka ware masa a hukumance, yayin da kwamishinonin hukumar uku da aka ware wa
riyal dubu goma sha biyar da dari tara da ashirin da tara kowanensu sai ga shi
an biya su riyal dubu arba’in.
Tun a ranar 30 ga
watan Yuli ICPC ta gayyaci shugaban hukumar alhazan, Jalal Arabi, domin ya yi mata
bayani game da yadda hukumar ta gudanar da aikin Hajjin da ya gabata.
Wata sanarwa daga
hukumar ta ce an gayyace shi ne kawai bisa tsari kamar yadda hukumar ta saba yi
duk bayan kowane aikin Hajji.
Tun da farko naira
miliyan hudu da dubu dari tara ne hukumar ta tsayar a matsayin kuɗin kujerar
zuwa aikin Hajjin da maniyyata za su biya, amma sai ta mayar da shi miliyan shida
da dubu dari takwas tana mai ɗora alhakin kan karyewar darajar naira.
Bayanin ya kara
da cewa an gano zunzurutun kudin da yawansu ya kai riyal miliyan takwas da dubu
dari shida da sha hudu da aka cire daga cikin naira biliyan 90 da
gwamnatin Najeriya ta bayar da aka canza su zuwa dalar Amurka inda suka kama
dala miliyan sittin da biyu da dubu dari uku da bakwai da dari da sittin da
hudu, da kuma aka saka su asusun ajiyar hukumar aikin hajjin da ke Saudiyya.
Kuma har yanzu ita kanta hukumar aikin hajjin ta kasa yin
cikakken bayanin yadda sauran kudaden suka yi batan-dabo.
Ba ya ga biyan
wasu kamfanoni da ke kasar Saudiyya miliyoyin kudaden da ba a san takamaiman
aikin da suka yi ba.
A kwanan baya a hirarsa da BBC, Sanata Ibrahim Abdullahi Dan Baba, tsohon
wakilin Sokoto ta Kudu a Majalisar Dattijai ta Najeriya ya ce irin badaƙalar
da bincikensu ya gano game da ayyukan wasu daga cikin jami'an Nahcon, ya hada
da badakalar kama wa mahajjata
dakunan kwana a otal da ya wuce kima inda a maimakon a kama na kwana 40 sai a
kama na kwana 90 domin a saka wasu daga baya a yi kashe-mu-raba tsakanin NAHCON
da masu otal-otal din.