Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/10/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/10/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. 'Har yanzu ba a kammala tantance mutanen da Tinubu ya yi wa afuwa ba'

    Ministan shari'a na Najeriya Lateef Fagbemi ya ce jerin sunayen mutanen da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yi wa afuwa na a 'matakin ƙarshe' na tantancewa, inda ya ƙunshi dubawa da nazari kan mutanen da ke ƙunshe a ciki.

    A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne shugaba Tinubu ya yi wa mutane 175 da aka kama da laifi afuwa, bayan samun amincewa daga majalisar magabata ta ƙasar.

    Daga cikin mutanen da shugaban ya yafe mawa akwai mutumin da ake wa kallon ɗaya daga cikin ƴan kishin ƙasa mafiya shahara Herbert Macauly, da tsohon ɗan majalisar wakilai Faruk Lawan da kuma Mamman Batsa, tsohon manjo-janar na soja wanda aka zartar wa hukuncin kisa a shekara ta 1986 bisa zargin kitsa juyin mulki.

    Sai dai afuwar ta janyo martani daga sassan ƙasar, inda aka yi zargin cewa jerin waɗanda aka yi afuwar ya ƙunshi waɗanda aka yanke wa hukunci bisa laifin safarar ƙwaya da masu haƙar ma'adanai ta haramtacciyar hanya.

    Wasu na ganin cewa wasu daga cikin mutanen ba su cancanci samun afuwar shugaban ƙasar ba saboda girman laifin da suka aikata.

    Ɗaya daga cikin waɗanda afuwar tasu ta janyo zazzafar muhawara ita ce Maryam Sanda, wadda aka yanke wa hukuncin kisa bisa laifin kashe mijinta Bilyaminu Bello.

    Sai dai a wata sanarwa da ministan shari'a Lateef Fagbemi ya fitar a yau Alhamis, ya ce babu wani da ake tsare da shi a gidan yari da aka sako, a cikin jerin waɗanda shugaban ƙasar ya yi wa afuwa.

    Sanarwar ta ƙara da cewa: "Batun yana a mataki na ƙarshe, wanda ya ƙunshi sake yin duba na tsanaki domin tabbatar de cewa duk sunayen da aka gabatar sun cika ƙa'idojin da aka gindaya kafin ba da izinin sakin su".

  2. An ƙayyade yawan kayan da mahajjatan Najeriya za su ɗauka a baɗi

    Hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya ta ƙayyade cewa mahajjatan ƙasar na da damar ɗaukar jakkuna biyu ne masu nauyin kilo 23 kowace, da kuma jakka ɗaya da za su riƙe a hannu sa'ilin shiga jirgi a lokacin aikin hajjin shekara ta 2026.

    Hukumar ta cimma wannan matsaya ce a lokacin wani taro da ta yi da shugabannin hukumomin alhazai na jihohi da kamfanoni shirya tafiye-tafiye yau Alhamis a Abuja.

    Hukumar ta shirya taron ne a ƙoƙarin sake nazari kan kuɗin hajji da ta sanar a baya da kuma lokacin gudanar da shirye-shiryen aikin na shekara mai zuwa.

    Sai dai jim kaɗan bayan hakan shugaban ƙasar Bola Tinubu ya umarci hukumar da ta sake nazari domin nemo hanyar rage kuɗin.

    A bayanin da shugaban hukumar ya yi wa BBC a baya, kuɗin aikin hajjin 2026 daga Najeriya zai kama ne daga naira 8,118,333.67 zuwa naira 8,561,013.67, dangane da ɓangaren ƙasar da maniyyaci zai tashi.

  3. Na yi tattaunawa mai amfani da Putin - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce tattaunawar da ya yi da shugaban Rasha Vladimir Putin ta waya ta yi amfani sosai, a ci gaba da ƙokarin da yake yi na sasantawa kan rikicin da ke wakana tsakanin Ukraine da Rasha.

    Bayan kammala wayar, Trump ya ce sun amince a yi wata ganawa tsakanin manyan jami'an gwamnatin Rasha da Amurka a mako mai zuwa, kafin daga baya kuma a yi wata ganawar ta gaba da gaba a birnin Budapest na ƙasar Hungary.

    An yi tattaunawar ta waya ne kwana ɗaya gabanin ziyarar da shugaban Ukraine Volodimyr Zelensky zai kai zuwa Amurka a gobe Juma'a domin neman ƙarin tallafi.

    Waya ta tsawon awa biyu

    Mai magana da yawun fadar shugaban Amurka, Karoline Leavitt ta bayyana cewa Putin da Trump sun kwashe "sama da awa biyu ne a kan waya".

    Lokacin da ta yi magana da manema labarai a birnin Washington, Leavitt ta sake nanata da dama daga cikin abubuwan da Trump ya bayyana a shafinsa na sada zumunta, cewar "tattaunawar ta yi amfani" kuma akwai "ci gaba sosai."

    Za a ci gaba da tattaunawa idan Shugaba Zelensky ya isa fadar White House a gobe Juma'a, in ji ta, inda ta ƙara da cewa Trump "ya cancanci dukkan yabo" a ƙoƙarin samar da zaman lafiya, jim kaɗan bayan nasarar yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

  4. 'Ƴanbindiga sun kashe jami'an tsaro takwas a Zamfara'

    Ƴan bindiga sun kashe jami'an ƴansanda da Askarawa takwas a hanyar Funtua zuwa Gusau.

    Cikin wani saƙo da gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya wallafa ashafinsa na Facebook, ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da ƴanbindigar suka yi wa jami'an kwanton-ɓauna.

    ''Allah (T) Ya ji ƙan su, Ya ba iyalai da 'yan'uwansu haƙurin wannan rashi'', kamar yadda gwamnan ya wallafa.

    Ba wannan ne karon farko da aka samu rahotonnin yi wa jami'an Askarawan kwanton-ɓauna a jihar Zamfara ba, wadda ke fama da matsalar tsaro.

  5. Trump zai yi waya da Vladimir Putin

    Shugaban Amurka Donald Trump na yin wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban Rasha Vladimir Putin - kwana ɗaya kafain ziyarar da shugaban Ukraine Volodimir Zelensky zai yi zuwa fadar White House domin neman ƙarin tallafi ga ƙasarsa.

    Trump na ci gaba da nuna ƙarin fusata game da ƙarin hare-haren Rasha a Ukraine.

    Hukumomin Ukraine sun ce Zelensky zai tattauna batun samar wa Ukraine makami mai linzami na Tomahawk mai cin dogon zango daga Amurka.

    A ranar Lahadi, Donald Trump ya ce zai iya faɗa wa Mista Putin cewa yana iya bai wa Ukraine tallafin makaman.

  6. Kamaru ta haramta duk wata zanga-zanga a birnin Douala

    Hukumomi a Kamaru sun ce sun haramta duk wata zanga-zanga a kan titunan babban birnin kasuwancin ƙasar wato Douala, har sai an rantsar da sabon shugaban ƙasar.

    Matakin ya zo ne bayan wasu manyan zanga-zanga da suka ɓarke a birnin mai tashar jiragen ruwa da kuma a wasu yankuna da ke kusa.

    An dai samu hargitsi a lardi na biyar na Douala inda cincirindon mutane suka taru a wajen ofisoshin hukumar zaɓe ta Elcam sanadin zarge-zargen cusa ƙuri’u a akwatunan zaɓe.

    Rahotanni sun ce mazaunan yankin da yawa ne suka taru suna yin alla-wadai da kura-kuren da aka samu da kuma neman a tabbatar da gaskiya a akwatunan da aka jefa ƙuri’u.

    Ƙungiyoyin fararen hula da masu sa ido a zaɓen sun yi alla-wadai da yunƙurin a matsayin wani farmaki kan ‘yancin gudanar da taruka.

    A lokaci guda kuma, ɗan takarar adawa Issa Tchiroma Bakari, ya fitar da wani jawabi ta bidiyo inda ya buƙaci masu sa ido a zaɓen su hana jirkita sakamakon zaɓen kuma su dage wajen kare muradin al’ummar ƙasar.

  7. Isra'ila ta mayar da ƙarin gawarwakin Falasɗinawa Gaza

    Isra'ila ta mayar da ƙarin gawarwakin Falasɗinawa sama da 30 zuwa Gaza, kamar yadda ma'aikatar lafiya da ke ƙarƙashin Hamas ta tabbatar.

    Ƙungiyar agaji ta Red Cross ce ta shiga tsakani wajen mayar da gawarwakin, kamar yadda ma'aikatar lafiyar ta Gaza ta wallafa a shafinta na sada zumunta.

    Wannan ya sanya yawan gawarwakin Falasɗinawa da Isra'ila ta mayar Gaza zuwa 120, in ji sanarwar. Tare da cewa likitoci na aikin tantance gawarwakin domin miƙa su ga iyalansu.

    A ƙarƙashin yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma tsakanin ɓangarorin biyu, Isra'ila ta amince cewar za ta miƙa gawarwakin Falasɗinawa 15 a kan duk gawar ɗan Isra'ila da Hamas ta mayar wa Isra'ilar.

  8. Ƴansanda sun tarwatsa mutanen da ke alhinin rasuwar Odinga

    Ƴansandan Kenya sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa dubban mutanen da suka taru a babban filin wasan Nairobi domin yin bankwana da gawar Raila Odinga.

    An ji ƙarar hareb-hare, kodayake babu tabbacin ko ƴansandan sun yi amfani da harsashi ko kuma na roba.

    Dubban mutane ne suka taru a ƙofar shiga filin wasan, domin jiran isar gawar filin wasan.

    An kai gawar Odinga zuwa filin wasan daga Indiya, wurin da ya rasu.

  9. Majalisar dattawan Najeriya ta amince da Amupitan a matsayin sabon shugaban INEC

    Majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da Farfesa Joash Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zaɓen ƙasar bayan tantance shi.

    Bayan dogon lokaci da ya shafe yana amsa tambayoyin ƴanmajalisar daga ƙarshe sun amince da naɗin nasa.

    Amupitan ya isa majalisar ne da wuri, inda ya gaggaisa da wasu daga cikin ƴanmajalisar dattawan.

    Sabon shugaban ya samu rakiyar gwamnan jihar Kogi, Ahmed Ododo da wasu daga cikin manyan baƙi.

  10. Ƙungiyar ƴantawayen Houthi ta tabbatar da kisan babban kwamandan sojinta

    Ƙungiyar Ƴantawayen Houthi a Yemen ta ce an kashe babban kwamandan sojinta bayan ''kammala aikinsa''.

    Ƙungiyar dai ba ta fito ƙarara ta ɗora alhakin kisan, Muhammad Abd al-Karim al-Ghamari kan Isra'ila ba.

    A watan Agusta ne dai Isra'ila ta kai hare-hare ta sama kan Sanaa, babban birnin Yemen, da nufin kai wa manyan kwamandojin ƙungiyar ciki har da al-Ghamari.

    Firaiministan da gwamnatin Houthi ke jagoranta na daga cikin wadanda suka mutu a hare-haren.

    Kafin yanzu, ƙungiyar Houthi ta dage cewa al-Ghamari na raye.

    Isra'ila ta sha kai hare-hare kan maɓoyar ƙungiyar Houthi a Yemen domin mayar da martani kan hare-haren makamai masu linzami da ƙungiyar ta kai Isra'ila.

  11. Dubban mutane sun cika wurin da ake jana'izar Odinga

    Dubban mutane na ci gaba da tuɗaɗa zuwa babban filin wasa na Kasarani, inda za a yi jana'izar tsohon firaiministan Kenya Raila Odinga.

    Dandazon mutane daga rukunonin al'umma daban-daban ne suka cika filin wasan domin jiran isar gawar jagoran adawar ƙasar.

    Wasu daga cikin mutanen da suka tarbi gawar daga filin jirhi sun zarce kai-tsaye zuwa filin wasan domin halartar jana'izar.

    Odinga ya rasu ne ranar Laraba a wani asibitin Indiya da yake jinya.

  12. Fafaroma Leo ya soki ƙasashen duniya kan rashin kare mutane daga yunwa

    Fafaroma Leo ya soki duniya kan rashin kare miliyoyin mutane daga aukawa ƙangin yunwa.

    Yayin da yake jawabi a taron Samar da Abinci da aka gudanar a birnin Roma, Fafaroman ya yi kira ga mutane su sake tunani kan tsarin rayuwarsu.

    Fafaroma Leo ya ce yayin da duniya ke asarar ɗimbin abinci mai yawa, mutane da dama na fama da abin da za su ci.

    Ya lissafo ƙasashen Ukraine da Gaza da Afghanistan da kuma Yemen, inda ya ce yunwa ta yi katutu a cikinsu.

    Ya kuma faɗa wa taron cewa amfani da yunwa a matsayin makami babban laifin yaƙi ne.

    A ranar Laraba, Shirin Samar da Abinci na Majalisar Dinkin Duniya ya ce fiye mutum miliyan 300 ne ke fama da matsalar rashin abinci a duniya.

  13. Kotu ta ce a biya ADC da SDP diyya saboda 'tauye musu haƙƙi'

    Babbar kotun jihar Kaduna ta kori ƙarar da kwamishinnan ƴansandan jihar ya shigar da jam'iyyun ADC da SDP.

    Kotun ta bayyana ƙarar a matsayin ''tozarta alfarmar kotu''.

    Kotun ƙarƙashin jagorancin Maishari'a Murtala Zubairu ce haramcin taron siyasa ta kwamishinan ƴansandan jihar ya saka ya saɓa wa kundin tsarin mulki.

    Haka kuma kotun ta umarci rundunar ƴansandan ta biya jam'iyyun ADC da SDP diyyar naira miliyan 15.

    Maishari'a Zubairu ya ce ƴansandan sun yi amfani da ƙarfin da ya wuce hurumin da kundin tsarin mulki ya ba su wajen hana jam'iyyun siyasa gudanar da taro wanda ɗaya ne daga cikin ginshiƙin ƴancin da dokokin ƙasar suka ba su.

    Jam'iyyun sun shigar da ƙarar ne bayan wata tarzoma da ta faru a lokacin da jam'iyyar ADC ke gudanar da wani taro a Kaduna, cikin watan Agusta, wanda tsohon gwamnan jihar, Mallam Nasir El-Rufai ya halarta.

    A lokacin taron, wasu da ake zargi da kasancewa ƴandabar siyasa sun kai samame wurin taron, tare da far wa mutanen da ke taron da lalata dukiyoyi.

  14. Nnamdi Kanu na da lafiyar da zai iya fuskantar shari'a - Likitoci

    Tawagar ƙwararrun likitoci a Najeriya, ƙarƙashin jagoranci shugaban ƙungiyar Likitocin ƙasar, sun tabbatar da cewa rashin lafiyar da aka ce na damun Nnamdi Kanu ba wata babbar damuwa ba ce.

    Maishari'a, James Omotosho ne ya umarci tawagar likitocin ta duba lafiyar Kanu, bayan da lauyoyinsa suka yi iƙirarin cewa yana fama da wata jinya.

    Cikin rahoton binciken tawagar ƙwararrun likitocin, da aka miƙa wa kotu ranar 13 ga watan Oktoban da muke ciki, ya ce rashin lafiyar da ke damun Kanu ba mai barazana ba ce.

    Tawagar likitocin ta ce bayan auna lafiyar Kanu sun tabbatar da cewa za a iya ci gaba da yi masa shari'a, domin kuwa zai iya halartar kotu.

    Bayan karɓar rahoton, Maishari'a Omotosho ya ce kotun ta gamsu da rahoton don haka za a ci gaba da shari'ar.

  15. Majalisar Dattawan Najeriya na shirin tantance sabon shugaban INEC

    Nan gaba a yau ne Majalisar Dattawan Najeriya za ta tantance Farfesa, Joash Ojo Amupitan domin zama sabon shugaban hukumar zaɓen ƙasar INEC.

    Matakin na zuwa ne bayan Shugaba Tinubu ya aike wa majalisar wasiƙar buƙatar tantance shi.

    A makon da ya gabata ne dai majalisar magabatan ƙasar ta amince da naɗin Farfesa Amupitan a matsayin wanda zai jagoranci hukumar zaɓen ƙasar.

    Bayan tantancewa da amincewar majalisar dattawan, Shugaba Tinubu zai rantsar da shi a matsayin shugaban hukumar da ke kula da shirya zaɓukan ƙasar.

    A makon da ya gabata ne tsohon shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu ya sauka daga muƙamin bayan ƙarewar wa'adinsa.

  16. Daruruwan matafiya na jiran buɗe kan iyakokin Pakistan da Afghanistan

    Ɗaruruwan matafiya ne ke ci gaba da maƙale a kan iyakokin ƙasashen Pakistan da Afghanistan yayin da yarjejeniyar tsagaita wutar ƴakin ɓangarorin biyu ke shiga kwana na biyu.

    Ƴankasuwa sun ce ɗanyun kayayyakin da suka saro na ci gaba da lalacewa.

    Kawo yanzu dai babu rahoton saɓa yarjejeniyar daga duka ɓangarorin biyu, to amma ministan tsaron Pakistan, Khawaja Asif ya bayyana shakkun ci gaba yarjejeniyar bayan da ya zargi Indiya da haddasa faɗa, kodayake bai bayar da hujja ba.

    A baya-bayan ne dai faɗa ya ɓarke tsakanin ƙasashen biyu, bayan da Afghanistan ta zargi Pakistan da haddasa fashe-fashe.

    A nata ɓangare Pakistan na zargin Afghanistan da ɗaukar nauyin ƴanbindiga da ke kai wa jami'an tsaronta hare-hare.

  17. Duka shugabannin ƙananan hukumomin Bayelsa sun fice daga PDP

    Duka shugabannin ƙananan hukumomin jihar Bayelsa takwas sun sanar da ficewa daga jam'iyyar PDP, tare da nuna goyon bayansu ga gwamnan jihar Douye Diri da shi ma ya fice daga jam'iyyar.

    Shugabannin ƙananan hukumomin sun bayyana matakin ne da maraicen ranar Laraba a wani taron manema labarai na haɗin gwiwa da suka gabata a Yenagoa babban birnin jihar.

    A ranar Laraba da rana ne gwamnan jihar ya sanar da ficewa daga jam'iyyarsa ta PDP, tare da duka ƴan majalisar dokokin jihar ƙarƙashin jagorancin kakakin majalisar.

    Kawo yanzu dai gwamnan bai bayyana jam'iyyar da ya koma ba.

  18. An mayar da gawar Raila Odinga Kenya daga Indiya

    Gawar tsohon Firaiministan Kenya, Raila Odinga ta isa babban filin jirgin sama na JKIA da ke ƙasar.

    Shugaban ƙasar, William Ruto da tsohon shugaban ƙasa Uhuru Kenyatta da manyan jami'an gwamnati ne suka tarbi gawar tare da iyalan Raila.

    A jiya ne gwamnatin kasar ta aika da wakilai zuwa Indiya, inda ya mutu domin raka gawar zuwa gida.

  19. Amurka na da ƙwarin gwiwar cewa Hamas ba za ta saɓa yarjejeniya ba

    Jami'an Amurka sun yi watsi da ikirarin cewa Hamas ta saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra'ila ta hanyar ƙin bayar da dukkannin gawarwakin mutanen da ta yi garkuwa da su.

    Bincike da aka gudanar ya tabbatar da cewa gawarwaki biyu da Hamas ta miƙa a ranar Laraba na cikin waɗanda ta yi garkuwa da su amma babu sauran 19.

    Wani jami'in fadar White House ya ce za a ɗauki makwanni kafin zaƙulo gawawwakin su saboda girman barnar da aka yi a Gaza.

    Ya ƙara da cewa akawai lada da za a bai wa ƴan Gaza da suka bayar da bayanai kuma ana sa ran gudanar da binciken tare da masana daga Turkiya