Ƴanbindiga sun kashe ƴansanda shida a Kenya
Ƴanbindiga da ake zargin ƴan ƙungiyar Al-Shabaab ne sun kashe ƴansandan Kenya guda shida.
Ƴanbindiga sun kashe ƴansandan ne a wani hari da suka kai a sansaninsu da ke Garisa, kusa da iyakar ƙasar da Somalia.
Bayan waɗanda suka rasu, wasu guda huɗu sun jikkata, inda yanzu haka suke jinya a wani asibitin ƙasar.
Ƴan ƙungiyar Al-Shabaab dai suna kai farmakin kan mai uwa da wabi ne kan jami'an tsaro da fararen hula a ƙasar Kenya.