Zaɓen shugaban ƙasar Iran ya kai mataki zagaye na biyu, bayan da 'yan takara biyu da ke kan gaba a sakamakon suka gaza samun kashi 50 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen na ranar Juma'a.
Ɗan takara mai ra'ayin kawo sauyi, Massoud Pezeshkian, ya samu ƙuri'a miliyan 10 da rabi, kimanin kashi 42.5 na ƙuri'un, inda ya bai wa babban abokin fafatawarsa a zaɓen, Saeed Jalili mai ra'ayin riƙau - da ya samu kashi 38.6 - tazarar ƙuri'a miliyan guda.
To sai dai duk da haka bai samu adadin da ake buƙata don bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen ba.
An samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri'a a zaɓen, lamarin da masu aiko da rahotonni suka alaƙanta da raguwar farin jinin tsarin gwamnati a ƙasar.
Rahotonni na cewa kashi 40 cikin 100 na waɗanda suka cancanci kaɗa ƙuri'a ne suka fito zaɓen, adadi mafi ƙaranci da suka fito zaɓe a tarihin ƙasar.
A Iran dole ne duka 'yan takara su samu sahalewar majalisar magaba, wadda jagoran addinin ƙasar, Ayatoullah Ali Khamenei ke naɗa duka mambobinta.
A ranar Juma'a mai zuwa ne za a gudanar da zaɓen zagaye na biyun.
Zaɓen shugaban ƙasar ya taso ne bayan rasuwar tsohon shugaban ƙasar Ebrahim Raisi a wani hatsarin jirgi, lokacin wata ziyara a yankin arewacin ƙasar, cikin watan Mayun da ya gabata.