Wasu jami'an gwamnatin Amurka sun shaida wa kafar watsa labarai ta CBS News cewa gwamnatin ta amince da tsare-tsaren kai jerin hare-haren kan muradan kasar Iran da ke kasashen Syria da Iraqi.
Hare-haren za su kasance ne na 'yan kwanaki kamar yadda jami'an suka shaida duk da cewa ba a fayyace lokacin da za a kaddamar da hare-haren ba.
Wannan dai na zuwa ne bayan wani harin jirgi maras matuki da ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin Amurka guda uku a kasar Jordan kusa da iyakar Syria a ranar Lahadi.
Amurka ta zargin cewa mayakan sa-kai ne Islamic Resistence da ke goyon bayan Iran ne suka kai harin
Ana dai zaton cewa kungiyar da ke Iraq tana da kungiyoyi masu tayar da kayar baya da dama a cikinta wadanda ke samun tallafi da makamai da horo daga dakarun juyin-juya hali na kasar Iran na Revelutionary Guards.
Kungiyar ta dauki alhakin kai harin kan sojin na Amurka na ranar Lahadi.
To sai dai kasar Iran ta musanta hannu a harin wanda ya kuma jikkata sojin Amurkan 41 a sansaninsu da ake kira Tower 22.
Yayin wani taron manema labarai ranar Alhamis, Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin ya ce Amurka "ba za ta amince da hare-hare kan sojinta" ba.
"Za mu dauki dukkan matakan da suka dace wajen kariya ga Amurka da muradanmu da kuma al'ummarmu", in ji Lloyd. "Za mu mayar da martani a duk inda muka zabi yin hakan da kuma yadda muke son aiwatarwa."
To sai dai jami'an Amurkar ba su shaida wa kafar ta CBS News komai ba game da hakikanin lokacin da za a aiwatar da hare-haren. Sai dai jami'an sun ce za su kaddamar da hare-haren ne a lokacin da yanayin sararin samaniyya ya yi muni to amma dai kuma za tabbatar an kai hare-haren ido na ganin ido domin rage yawan mutuwar fararen hula.
A dai-dai lokacin da Amurkar ta sha alwashin mayar da martanin na harin jirgi maras matuki, shugaba Joe Biden da sauran jami'an tsaro sun ce Amurkar ba ta da burin fadada yaki da kasar Iran saboda gudun ta'azzarar rikici a yankin.
"Ba abin da nake son gani ba kenan," kamar yadda mista Biden ya shaida wa 'yan jarida a Fadar White House a farkon wannan makon.