Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Isra'ila ta amince a kai kayan gaji Gaza amma ta Masar

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Haruna Kakangi and Umar Mikail

  1. Mu zama lafiya

    Ƙarshen rahotonnin ke nan a wannan shafi na labarai kai-tsaye.

    Za mu kawo muku wasu sababbi da suka shafi rayuwarku gobe da safe kamar yadda aka saba.

    Kafin lokacin, kuna iya duba ƙasa domin karanta labaran da muka ruwaito musamman game da yaƙin da ake yi a Zirin Gaza tsakanin Hamas da Isra'ila.

    Umar Mikail da Mukhtar Bawa ne ke cewa mu zama lafiya.

  2. Daruruwan masu zanga-zanga sun yi sallah a wajen fadar firaministan Birtaniya

    Daruruwan masu zanga-zanga sun halarci wani taron nuna juyayi a wajen fadar Downing Street don mutanen da mummunar fashewar wani abu ta ritsa da su a wajen asibitin Al-Ahli Arab da ke Gaza.

    Masu zanga-zangar sun jurewa ruwan sama da maryacen Laraba, inda suka taru a Westminster suna daga kwalaye masu rubuce-rubuce kamar "a dakatar da kisan kiyashi" da kuma "a dakatar da luguden bama-bamai a Gaza".

    Daga nan, an gudanar da addu'o'i da Larabci, inda mahalartan suka shimfida tabarmin leda don yin sallah.

    Kamar yadda muka rika ba ku rahotanni a yayin wata ziyara da kai Isra'ila, Shugaba Joe Biden ya nuna goyon bayansa ga musanta duk wani hannu a fashewar da aka samu a asibitin na Gaza da Isra'ila ta yi.

    Yana cewa matakin nasa ya dogara ne a kan "bayanai" da ya gani daga ma'aikatar tsaron Amurka.

    Hamas dai ta dora alhakin abin da ya faru, wanda ya yi sanadin mutuwar daruruwan fararen hula a kan wani harin Isra'ila ta sama.

  3. Labarai da dumi-dumi, Masar ta amince da bude mashigar Rafah

    Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya amince da bude mashigar Rafah ga wasu manyan motoci kalilan dauke da kayan agaji zuwa Zirin Gaza, Shugaba Joe Biden ne ya sanar da haka.

    Da yake jawabi a cikin jirgin saman Air Force One yayin wata ziyarar bazata ga manema labarai na cikin jirgin, shugaban ya ba da karin haske ga 'yan jaridan game da tattaunawarsa da Shugaba Sisi.

    Ya bayyana cewa Shugaba Sisi ya amince ya bude mashigar Rafah, don bai wa motocin daukar kaya 20 na taimakon kayan jin kai zuwa Gaza.

    Biden ya ce: “Idan Hamas suka kwace su ko kuma suka ki bari su wuce … shi kenan.”

    “Muhimmin abu dai ne shi ne Shugaba Sisi ya cancanci yabo.”

    • Me ya sa mashigar Rafah a Gaza ke da muhimmanci
  4. Lokacin tsagaita wuta a yaƙin Isra'ila da Gaza bai yi ba - Gwamnatin Birtaniya

    Fadar gwamnatin Birtaniya ta Downing Street ta ce lokacin neman a tsagaita wuta a yaƙin da Isra'ila ke yi da Hamas bai yi ba.

    Mai magana da yawun Firaministan Birtaniya Rishi Sunak ya ce shugaban na ganin lokaci bai yi ba saboda "Isra'ila na yunƙurin ceto 'yan ƙasarta da 'yan ta'adda suka yi garkuwa da su".

    Tun da farko, 'yan majalisa fiye da 35 ne suka nemi firaministan ya taimaka wajen dakatar da zubar da jini da kuma samar da hanyoyin kai kayan abinci, da magunguna, da man fetur zuwa Gaza, waɗanda Isra'ila ta hana.

    Lokacin da yake amsa tambayoyi a majalisa, an tambayi Mista Sunak ko zai saka baki a kiraye-kirayen tsagaita wuta.

    Shi kuma sai ya amsa da cewa "Isra'ila na da haƙƙin kare kanta da al'ummarta, da kuma mayar wa 'yan ta'adda martani".

  5. Yaƙin Gaza: Masu zanga-zangar neman tsagaita wuta sun kutsa Majalisar Dokokin Amurka

    Ɗaruruwan masu zanga-zanga sun yi wa ginin Majalisar Dokokin Amurka tsinke suna kiran a tsagaita wuta a yaƙin da Isra'ila ke yi da Hamas a Zirin Gaza.

    Bayanai sun nuna cewa cikin masu zanga-zangar har da Yahudawa, inda suka shiga cikin farfajiyar ginin ɗauke da kwalaye masu saƙo iri-iri.

    An ga yadda jami'an tsaro suka dinga kama wasu daga cikin masu macin suna fita da su waje.

    Lamarin na zuwa ne yayin da Shugaba Joe Biden ke kan hanyar komawa gida bayan ya jaddada goyon bayansa ga hare-haren da Isra'ila ke kaiwa a ziyarar da ya kai birnin Tel Aviv.

  6. Harin Isra'ila ya faɗa kusa da asibiti a Gaza, a cewar PRC

    Wani hari da Isra'ila ta kai ya faɗa kusa da Asibitin al-Quds a unguwar al-Hawa da ke Birnin Gaza, a cewar ƙungiyar agaji ta Red Crescent (PRC) ta Falasɗinu.

    PRC ta ce mutum kusan 8,000 ne ke fakewa a asibitin, wanda Isra'ilar ta taɓa kai wa hari a baya kuma ta lala shi a 2009.

    Wani bidiyo da ƙungiyar ta wallafa a dandalin X ya nuna yadda wuta ta tashi a tsallaken asibitin bayan dirar makamin.

    An kashe ma'aikatan agaji kusan 16 tun bayan fara kai hare-hare a kan Zirin Gaza ranar 7 ga watan Oktoba.

  7. Amurka za ta bai wa Falasɗinawa tallafin dala miliyan 100 - Biden

    Yayin ziyarar da ya kai Isra'ila, Shugaban Amurka Joe Biden ya yi yunƙurin bayyana ra'ayinsa game da damuwar Falasɗinawa da sauran Larabawa.

    Ya yi alƙawarin dala miliyan 100 a matsayin tallafin da Amurka za ta ba wa Zirin Gaza da kuma Gaɓar Yamma da Kogin Jordan (West Bank).

    Kazalika, shugaban ya bai wa Isra'ila shawara yayin da take shirin ƙaddamar da hari ta ƙasa a Gaza.

    "Ya kamata Isra'ila ta daddale ƙarara kan abin da take so ta cimma a wannan yaƙi..kuma hakan na buƙatar yin nazari kan ko hanyar da take kai za ta ba ta damar cimma wannan manufar," in ji Biden yayin wani jawabi.

    Wannan gargaɗi ne ƙarara ga gwamnatin Firaminista Netanyahu cewa kada ta wuce gona da iri, a cewar wakilin sashen diflomasiyya na BBC Paul Adams.

  8. Me bidiyo zai iya fada game da abin da ya fashe a asibitin Gaza?

    Sashen BBC Verify mai tantance bayanai, yana kokarin bankado wanne ne, ko ba wanne ba, da aka san ya faru game da abin da ya fashe a asibitin Al-Ahli.

    Tashin abin fashewar ya faru ne da misalin karfe 7 na yamma agogon Gaza ranar Talata. Hotunan bidiyo a shafukan sada zumunta sun rika nuna abin da ga alama fashewar da aka samu ce amma daga fuskoki daban-daban.

    BBC ta yi kokarin kwatanta bayanan gine-gine da tsarin ginin asibitin Al-Ahli da hotunan tauraron dan'adam da ake samu a bainar jama'a, don tabbatar da cewa asibitin ne wurin da fashewar ta faru.

    Mun tuntubi adadin kwararru don tabbatar da ko ana iya amfani da shaidun bidiyon da ake da su, wajen fayyace abin da ya haddasa fashewar.

    Zuwa yanzu sakamakon binciken bai kammala ba.

    Daya daga cikin kwararrun ya ce shaidun da aka gani zuwa yanzu ba su yi daidai da abin da za a sa ran gani ba a ire-iren hari ta sama da Isra'ila ta saba kai wa. Wani kwararren kuma ya ce shaidar kamar tana nuna sanadin abin fashewar daga wani makamin roka ne da ya yi kuskure ya fada a wurin ajiye motoci.

    Kwararru da dama da muka zanta da su, ba su bayyana aniyar gabatar da wani hange da suke da shi kan abin da ya faru ba.

  9. Amurka ta ƙi amincewa da ƙuri'ar tsagaita wuta a Gaza

    Amurka ta yi amfani da ikonta a kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNSC) wajen ƙin amincewa ƙuri'ar neman tsagaita wuta a yaƙin da Isra'la ke yi da ƙungiyar Hamas a Zirin Gaza.

    An kasa cimma matsaya ne a kan ƙudirin da ƙasar Brazil ta gabatar a yau Laraba bayan mambobin kwamitin sun yi watsi da daftarin da Rasha ta gabatar a jiya.

    Amurka ta ce ƙudirin bai ambaci haƙƙin Isra'ila ba na kare kanta daga hare-haren ƙungiyar Hamas da sauran 'yan gwagwarmayar Falasɗinawa.

    Ga yadda mambobin kwamitin 15 suka kaɗa ƙuri'ar:

    Masu goyon bayan ƙudirin:

    Faransa, China, Albania, Brazil, Ecuador, Gabon, Ghana, Japan, Malta, Mozambique, Switzerland, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa

    Waɗanda ba su goyon baya:

    Amurka

    Waɗanda suka ƙaurace wa ƙuri'ar:

    Birtaniya, Rasha

  10. Labarai da dumi-dumi, Isra'ila ta amince a kai kayan gaji Gaza amma ta Masar

    Isra'ila ta ce ba za ta hana kai kayan agaji cikin Zirin Gaza ba amma sai dai a bi ta Masar mai maƙwabtaka da zirin.

    Wata sanarwa daga ofishin Firaminista Benjamin Netanyahu ta ce abinci da ruwa da magunguna kaɗai za ta bari a shiga da su.

    "Ba za mu hana shigar da kayan agaji daga Masar ba matuƙar dai abinci ne da ruwa da kuma magunguna zuwa ga fararen hula da ke kudancin Gaza," in ji sanarwar.

    Ta ƙara da cewa "ba za mu bar kayan agaji su shiga ta ɓangaren ƙasarmu ba har sai an sako mutanenmu da aka yi garkuwa da su".

  11. Zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa ta barke a Gabar Yamma da sauran yankin

    Zanga-zanga ta barke a yankin Gabar Yamma da ke karkashin mamayen Isra'ila da kuma a Jordan da Iran da Tunisiya da Lebanon da kuma tun farko a Turkiyya.

    Zanga-zangar ta zo ne bayan tashin wani abin fashewa cikin daren jiya a asibitin Al-Ahli Arabi da ke Gaza.

    Hamas ta zargi Isra'ila da kai harin ta sama, sai dai Isra'ila ta gabatar da shaidar da ta ce tana nuna lamarin ya faru ne sanadin wani makami mai linzami da wata kungiyar Falasdinawa 'yan ta-da-kayar-baya ta harba a Gaza amma ya yi kuskuren hanya.

    Ga wasu daga cikin hotunan zanga-zangar a fadin Gabas ta Tsakiya.

  12. Joe Biden na dab da barin Isra'ila

    Shugaban Amurka Joe Biden ya koma cikin jirginsa na Air Force One yayin da yake barin Isra'ila.

    Bayan saukarsa a birnin Tel Aviv a safiyar yau, ya shafe kusan awa takwas yana tattaunawa da jami'an gwamnati da iyalai, da kuma Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

    Sai dai kuma bai gana da shugabannin Larabawa ba na ƙasashen Masar da Jordan da kuma Falasɗinawa bayan sun soke ganin sa a yau ɗin.

    Amma an ce zai yi waya da su daga cikin jirgin.

  13. Phillips zai fayyace makomarsa nan gaba a Man City

  14. Takunkuman Ecowas ba su dace ba - Mata masu zanga-zanga a Nijar

    A jamhuriyar Nijar, a yau ne wasu mata suka gudanar da zanga-zangar zaman dirshen a gaban ofishin kungiyar raya ƙasashen Afirka ta Yamma (Ecowas ko Cedeao) don neman kungiyar ta cire takukuman da ta kakaba wa kasarsu bayan juyin mulkin 26 ga watan Yuli.

    Wannan ne karon farko tun bayan ɓarkewar hargitsin siyasa da wasu mutane suka je cibiyar Ecowas don yin zanga-zanga.

    Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma na shan suka daga al'ummar Nijar game da matakinta na sanya wa kasarsu takunkumai da kuma barazanar amfani da karfin soji don mayar da zaɓaɓɓiyar gwamnatin Shugaba Bazoum Mohamed da sojoji suka hambarar daga mulki.

    Ga karin bayani a rahoton wakiliyar BBC a birnin Niamey, Tchima Illa Issoufou:

  15. Biden: Muna nan tare da Isra'ila

    "Muna nan tare da ku, Isra'ila," a cewar Biden, ya kara da cewa Amurka "za ta ci gaba da goyon bayan ku a wadannan ranaku masu duhu".

    Isra'ila za ta kasance amintacciyar kasar dimokradiyya mai cike da tsaro ga al'ummar Yahudawa "a yau, da gobe da kuma har abada", in ji shi.

    "Ubangiji ya kare dukkan wadanda ke aiki don tabbatar da zaman lafiya. Ubangiji ya kare wadanda har yanzu ke wuraren da za a iya cutar da su."

  16. Bitar bayanai cikin sauri daga jawabin Biden

    Shugaba Biden ya gabatar da jawabi - cikin sauri ga takaitattun bayanai masu muhimmanci daga ciki.

    • Game da tashin abin fashewa a asibitin Gaza cikin daren jiya, ya ce ya yi "takaici da bacin rai" a kan dumbin rayukan da aka rasa - kuma shaida na nuni ga "wani makamin roka da wata kungiyar 'yan ta'adda a Gaza ta harba amma ya kuskure"
    • Game da kayan agaji, ya ce ya nemi majalisar tsare-tsaren yaki ta Isra'ila ta amince da kai da kai "kayan taimakon jin kai don kubutar da rayukan fararen hula da ke Gaza" bisa fahimtar cewa za su je ga fararen hula ne amma ba Hamas ba - kuma Isra'ila ta amince kayan agaji za su iya "fara shiga Gaza daga kasar Masar"
    • Game da tallafin kudi daga Amurka, ya sanar da tallafin dala miliyan 100 "sabon tallafin kudi na Amurka don taimakon jin kai a Gaza da kuma Gabar Yamma" - akwai kuma alkawari na yiwuwar samar da kunshin tallafin tsaro "da ba a taba yin irinsa ba" ga Isra'ila, wanda ya ce zai nemi Majalisar Amurka ta amince da shi nan gaba cikin makon nan
    • Ga al'ummar Isra'ila, ya ce kasarsu an "kafa ta ne ta kasance wani wuri mai aminci ga Yahudawan duniya" kuma ya yi alkawarin cewa Amurka za ta yi "duk abin da take iya yi cikin ikonmu" don cimma wannan buri
  17. Majalisar wakilai ta umarci a yi bincike kan kuɗaɗen yaƙi da annobar korona

    Majalisar wakilkan Najeriya ta umarci kwamitinta da ke kula da yadda ake kashe kuɗaɗen gwamnati ya gudanar da bincike a kan yadda ma`aikatu da hukumomin ƙasar suka kashe kuɗaɗen da aka bayar na yaƙi da cutar korona.

    Majalisar ta dauki wannan matkin ne sakamakon wani ƙuduri da Hon Nyampa Dauda Zakaria ya gabatar, wanda ya yi zargin cewa an yi facaka wajen kashe kusan naira biliyon dari biyu da gwamnati ta bayar don yaƙi da annobar.

    Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Ibrahim Isa

  18. Magoya bayan Ingila na hakika ba sa yi wa dan wasa ihu - Maguire

  19. Yau ce ranar ɗaukewar jinin al'ada ga mata ta duniya

    Yau ce rana ta musamman ta duniya da aka ware don duba batutuwan da suka shafi shekarun daukewar jinin al'ada ga mata.

    Mataki ne na manyantar mace, wato lokaci ne da za ta daina yin jinin al'ada da kuma haihuwa.

    Taken ranar na wannan shekarar shi ne, ''cututukan da suka alakanci zuciya''.

  20. Kenya ta fara kwashe 'yan kasarta daga Isra'ila

    Kenya ta fara kwashe 'yan ƙasarta daga Isra'ila bayan barkewar yaki kwanaki 10 da suka gabata.

    Kashin farko na mutane 11 da aka kwashe ana sa ran isarsu nan gaba a ranar Laraba, a cewar Roseline Njogu, wata babbar jami'a mai kula da harkokin Ƙasashen waje a ma'aikatar harkokin wajen Kenya.

    A halin yanzu, akwai ƴan ƙasar sama da 500 da suka yi rajista da ofishin jakadancin Kenya a Isra’ila, tare da wasu adadi mai yawa daga cikinsu da ke zaune a yankunan da rikicin bai shafa ba kuma ba a bar su ba sakamakon tashin hankalin.

    Yaƙin ya fara ne a ranar 7 ga watan Oktoba da wani hari da ba a taba gani ba a kan al'ummomin Isra'ila da ke kusa da Zirin Gaza daga mayakan Hamas na Falasɗinawa.

    Isra'ila ta mayar da martani da farmaki a kan Gaza.