Wani ayarin manyan jami'an Saudiyya yana yankin Gabar Yamma da Kogin Jordan da ke karkashin mamaya karon farko tun bayan kwace yankin da Isra'ila ta yi daga kasar Jordan a yakin 1967.
Sa'o'i bayan isar jami'an, ministan yawon bude ido na Isra'ila shi ma ya sauka a Saudiyya, don halartar wani taron Majalisar Dinkin Duniya.
Haim Katz ya zama ministan Isra'ila na farko da ya jagoranci wani rukunin jami'an kasar zuwa wata ziyara a kasar Saudiyya, kamar yadda ofishinsa ya ce.
Muhimman ziyarce-ziyarcen na zuwa ne bayan shugabannin Saudiyya da na Isra'ila sun furta kalaman alheri game da kokarin kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu.
Amurka a baya-bayan nan ta shiga tsakani don cimma sasantawa mai sarkakiya tsakanin manyan kawayenta biyu na yankin.
Wata yarjejeniya tsakanin kasashen mafi karfi a yankin za ta kawo wani sauyin bagtatan a siyasar Gabas ta Tsakiya kuma za ta samar da wata babbar nasara a manufar Amurka ta hulda da kasashen waje.
A ranar Talata da safe, babban jakadan Saudiyya na farko a yankin Falasdin, Nayef al-Sudairi wanda kuma shi ne jakadan kasar Jordan ya tafi a mota zuwa Gabar Yamma da Kogin Jordan ta mashigar Karama a wata ziyarar kwana biyu.
Isra'ila ce take iko da mashigin a kan iyaka, kuma sai ta bayar da izini gabanin isarsa.
Ma'aikatar harkokin wajen Falasdin ta bayyana lamarin a matsayin "wani muhimmin abin tarihi" a huldar da ke tsakaninsu da gwamnatin Riyadh.
An yi wa jami'in diflomasiyyar na Saudiyya maraba da kade-kade a Ramallah, inda Hukumar Falasdin take da shalkwata.
A fadar shugaban, Nayef a-Sudairi ya duba faretin ban girma daga dakarun da suka jeru a layi don gaishe shi, yayin da aka buga taken kasar Saudiyya da na al'ummar Falasdin.
Daga nan sai ya mika takardun kama aikin jakadanci ga Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas yayin wani biki.
Da yake jawabi ga manema labarai,
Mallam Sudairi ya yi kokarin jaddada tabbaci ga al'ummar Falsdinawa a kan duk wani ci gaba. Ya buga misali da wata hirar da ba-sabon-ba da Yarima Mai jiran Gado Mohammed bin Salman ya yi da tashar talbijin ta Fox News.
Yarima Mohammed ya ce "kullum muna kara kusantar" cimma yarjejeniya don daidaita alaka tsakanin kasarsa da Isra'ila, inda ya kara da cewa batun al'ummar Falasdin har yanzu yana da "matukar muhimmanci" a wani bangare na tattaunawa.
-
Majalisar Ɗinkin Duniya ta nemi jin matsayin kotun duniya kan mamayen Isra'ila a Falasɗinu