Tawagar wakilan ƙasashen Birtaniya da Amurka da Ireland da Jamus da Faransa da ƙungiyar Tarayyar Turai ta EU a zaɓen Saliyo da za a gudanar, sun yi kira ga al'ummar ƙasar da su guje wa tashin hankali, sannan su martaba ra'ayoyin juna, tare da guje wa yin kalaman da za su tunzura juna da kawo rarrabuwar kai, a yayin da ake shirin gudanar da babban zaɓen ƙasar ranar Asabar da ke tafe.
A wata sanarwar haɗin gwiwa da wakilan ƙasashen suka fitar, sun bayyana damuwarsu kan rahotonnin rikice-rikicen siyasa da ake samu a ƙasar da ke yammacin Afirka.
Wakilan sun yi kira ga jam'iyyun siyasa da 'yan takara da su yi biyayya ga yarjejeniyar zaman lafiya da suka sanya wa hannu cikin watan da ya gabata.
Yarjejeniyar dai ta buƙaci jam'iyyu da 'yan takarar da su riƙa yin kira ga zaman lafiya, tare da gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali, sannan su garzaya kotuna domin gabatar da ƙorafin da suke da shi game da zaɓen.
Tawagar wakilan manyan ƙasashen yamman sun jaddada goyon bayansu kan gudanar da ingantacce kuma sahihin zaɓe cikin kwanciyar hankali, kamar yadda al'ummar ƙasar ke buƙata.
Ana samun ƙaruwar zaman ɗar-ɗar a fadin ƙasar, yayin da mazauna Freetown babban birnin ƙasar ke tururuwar sayen abinci da sauran kayayyaki a kasuwanni, sakamakon fargabar ɓarkewar rikici a ƙasar.
Hakan na zuwa ne bayan da aka samu wata arangama tsakanin jami'an tsaro da magoya bayan babbar jam'iyyar adawar ƙasar ranar Laraba, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda.
Ƙasar Saliyo na fuskantar matsin tatalin arziki, da tsadar rayuwa, inda talauci da rashin aikin yi tsakanin al'umma ke ci gaba da ƙaruwa, baya ga hauhawar farashin kayayyaki.
'Yan takara 13 ne za su fafata a zaɓen, to sai sai masu hasashe na ganin zaɓen zai fi zafi tsakanin manyan 'yan takar biyu, wato shugaban ƙasar Julius Maada Bio da ke neman wa'adin mulki na biyu, sai kuma Samura Kamara na babbar jam'iyyar adawa ta All People's Congress wato APC.