Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Kotu ta umarci DSS su bar Emefiele ya gana da iyalansa

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan dake faruwa a Najeriya da sauran ƙasashe

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Abdullahi Bello Diginza, Mukhtar Adamu Bawa and Haruna Kakangi

  1. Sojoji sun ƙalubalanci Dokubo ya bayyana sunayen masu satar ɗanyen man fetur

    Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ƙalubalanci tsohon jagoran masu fafutika na yankin Neja Delta, Mujahid Asari Dokubo da ya bayyana sunayen jami’an da ke satar ɗanyen mai.

    A ranar Juma'a ne Asari Dokubo ya yi zargin cewa akwai hannun sojojin Najeriya na ruwa a yawancin laifukan satar mai da ake samu a yankin Neja-Delta.

    Dokuba ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa bayan ganawarsa da shugaba Bola Tinubu.

    Sai dai yayin da yake mayar da martani, mai magana da yawun rundunar sojin ruwan Najeriya, Commodore Adedotun Ayo-Vaughan, ya bayyana zargin a matsayin maganar da babu gaskiya a cikinta.

    Ya ce ɓarayin mai sun fusata ne saboda sojojin ruwan Najeriya da ɗaukacin sojojin na ci gaba da hana su hanyoyin da za su yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta hanyar wani shiri na dakatar da ayyukan ɓarayi.

    Ya ci gaba da cewa rundunar sojin ruwa tare da hadin guiwar masu ruwa da tsaki za su ci gaba da hana ɓarayin danyen mai hanyoyin yin zagon kasa ga tattalin arzikin Najeriya.

    A wata hirar da ya yi da jaridar Daily Trust, Ayo-Vaughan,ya ce “Ya kamata ya kawo sunayen. Rundunar sojin ruwan Najeriya na buƙatar samun sunayen waɗanda abin ya shafa domin rundunar ba za ta ɗauki duk wani nau’in aikata laifuka ba ko da kuwa ta kai girman sata irin yadda Asari Dokubo yake zargin''.

    “Saboda haka, sojojin ruwa suna yaƙar satar mai. Duk wanda zai yi irin wannan zarge-zargen, sai ya kawo sunayen. Shi (Dokubo) yana yankin Neja-Delta, ai yana da yara a yankin Neja Delta''.

  2. Gwamnatin Mali ta ce ba ta ga amfanin dakarun Majalisar Ɗinkin Duniya ba

    Ministan harkokin wajen kasar Mali ya bukaci kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ya gaggauta janye aikin wanzar da zaman lafiya na MDD wanda a cewarsa ya gaza.

    Dubban sojojin Majalisar Dinkin Duniya sun kwashe sama da shekaru goma a Mali amma sun kasa dakile yaduwar hare-haren masu jihadi da suka bazu zuwa kasashe makwabta.

    Ministan harkokin wajen Mali, Abdoulaye Diop ya ce tsaro a kasar ya taɓarɓare sosai fiye da shekaru goma da suka gabata, ya bukaci kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ya janye daukacin dakarun MDD da aka fi sani da MINUSMA ba tare da ɓata lokaci ba.

    Shirin wanzar da zaman lafiyar mai cin kuɗi dala biliyan daya a kowace shekara na fuskantar suka daga bangarori daban-daban na kasar inda a yanzu haka sojoji suka kwace mulki a wani juyin mulki.

    Sun yanke hulda da kawayen kasar Mali na asali ciki har da Faransa, kuma sun kulla sabuwar cudanya da Rasha.

    Sama da dakaru dubu ne na kungiyar Wagner aka jibge a kasar domin taimakawa wajen yaki da kungiyoyi masu ikirarin jihadi.

    Masu sukar rundunar Majalisar Dinkin Duniya sun ce ba ta da wani tasiri. Wasu na fargabar cewa idan suka tafi, masu ikirarin jihadi ba za su fuskanci matsin lamba sosai ba.

  3. Dokubo Asari ya zargi sojoji da hannu wajen satar ɗanyen man fetur a Najeriya

    Fitaccen shugaban yankin Neja Delta, Asari Dokubo, ya zargi sojojin Najeriya da laifin satar mai a kashi 99 cikin 100 a kasar.

    Dokubo ya yi wannan zargin ne bayan wata ganawar sirri da shugaban kasa Bola Tinubu a ofishin sa ranar Juma’a.

    Ya bayyana cewa shugaban kasar ya yi alkawarin gudanar da bincike kan zargin badakalar man fetur da wasu fitattun kwamandojin ruwa wadanda suka gawurta suke gudanarwa, kuma ya yi alkawarin daukar kwararan matakai don dakatar da wannan mummunar aikin.

    Dokubo ya kara da cewa, akwai wadansu jiga-jigai da ke aiki daga Abuja, yana mai shan alwashin cewa wadannan mutanen yanzu sun hadu da wanda ya fi karfin su kuma nan ba da jimawa ba za a fara tasa keyar irin waɗannan mutane zuwa gidan yari.

    Ya ce za a iya amfani da yara masu yi masa aiki wurin yaki da wananan mummunar aikin.

    Tsohon shugaban masu tayar da kayar bayan ya ce talakawan yankin Neja-Delta da ake zargi da satar mai ba su da ƙwarewar yin sata irin na zamani.

    A cewarsa, yadda barayin man fetur ke gudanar da ayyukansu na aikata muggan laifuka, ya hana al'ummar yankin Neja-Delta gudanar da rayuwarsu, kuma hakan laifi ne na cin zarafin bil’adama.

    Dokubo ya kuma yi zargin cewa wani abin kunya ne ga sojoji su ce ba su da isassun kayan yaki da za su magance matsalar tsaro, inda ya zarge su da yin watsi da makamansu ga ‘yan ta’addan, lamarin da ya ci gaba da hura wutar rikicin.

  4. Kotu ta umarci DSS su bar Emefiele ya ga iyalansa

    An umarci babban daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da hukumar DSS din kanta da su gaggauta bai wa gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) da aka dakatar, Godwin Emefiele damar ganawa da lauyoyinsa da iyalansa ba tare da ɓata lokaci ba, kamar yadda tsarin mulki ya tanadar.

    Umarnin ya fito ne daga mai shari’a Hamza Muazu na babbar kotun birnin tarayya da ke zamanta a Maitama Abuja a ranar Juma’a.

    Lauyan Emefiele JB Daudu ya sanar da kotun cewa ya rubuta wa hukumar DSS wasiku, musamman a ranar 14 ga watan Yuni domin neman ƙarin umarni daga wurinsa, amma hukumar DSS ta ƙi amsa buƙatar.

    A ɗaya ɓangaren kuma lauyan waɗanda ake ƙara na biyu da na uku, I. Awo, ya shaida wa kotun cewa hukumar DSS ba ta da hurumin ƙin amincewa da wannan buƙata, kuma yin hakan ba daidai ba ne.

    Sai dai ya bayyana tabbacin hukumar tsaron za ta bi umarnin kotu tare da bai wa lauyoyin da aka lissafa da kuma iyalan Emefiele damar ganin sa.

    Hukumar DSS ta kama Emefiele a ranar Asabar, sa’o’i kaɗan bayan shugaba Bola Tinubu dakatar da shi daga muƙaminsa a yammacin Juma’a.

  5. Boko Haram da ISWAP na ƙara samun fasahohin zamani don ayyukansu

  6. Amurka ta yi Allah-wadai da tu'annatin da ake yi a Sudan

    Amurka ta yi tir da ayyukan assha da ake tafkawa, waɗanda suka haɗa da fyade da kisa na ƙabilanci, waɗanda ake jinginawa da mayaƙan ƙungiyar RSF da masu alaƙa da ita a Yammacin Darfur.

    Ma'aikatar hulɗa da ƙasashen waje ta Amurka ta ce duk da dai an fi alaƙanta ayyukan asshan da ƙungiyar RSF amma dukkanin ɓangarorin biyu na da hannu a ciki.

    Ma'aikatar ta ce sojojin gwamnatin Sudan sun gaza kare fararen hula bayan takalo faɗan, lamarin da ya haifar da samuwar ƙungiyoyi na ƙabilanci.

    Sanarwar ta ce "Tu'annatin da ake yi yanzu haka a Yammacin Darfur da wasu yankuna tamkar maimaci ne na mummunan al'amarin da ya faru a 2004 a yankin Darfur, wanda ya sanya Amurka ta ayyana lamarin a matsayin kisan-kiyashi."

    Sanarwar na zuwa ne bayan da dakarun Sudan suka zargi sojojin RSF da kamawa tare da hallaka gwamnan jihar ta Yammacin Darfur, Khamis Abdalla.

    Tuni RSF ta musanta zargin.

    Kimanin mutum 1,000 ne ƙungiyoyi masu goyon bayan dakarun RSF a Yammacin Darfur suka hallaka, kamar yadda masu sanya ido a ƙasar suka tabbatar.

    Yaƙin wanda ya ɓarke tsakanin dakarun gwamnati da na ƙungiyar RSF a ranar 15 ga watan Afrilu ya raba sama mutum miliyan biyu da gidajensu.

  7. Boko Haram sun kashe mazauna wani ƙauyen Borno su 15

    Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kashe aƙalla mutane 15 a hare-haren haɗin gwiwa da suka kai wasu ƙauyuka biyu na ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

    Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa ‘yan ta’addan sun kai farmaki ne ƙauyen Kofa cikin tsakar dare inda suka fara harbe-harbe, wanda ya dauki kimanin sa’a guda.

    An samu labarin cewa sun kuma kai hari a Molai Kura da Molai Gana, inda suka yi wa wasu mutane yankan rago.

    An ba da rahoton cewa mazauna yankin da dama sun tsere daga gidajensu don samun mafaka a cikin daji.

    Wani jigo a ƙungiyar ’yan sintiri, Bukar Ali Musty, ya ce manoma na aikin gonakinsu a ƙaramar hukumar Jere cikin jihar Borno ne, a lokacin da "‘yan ta’addan suka kai musu hari" tare da sare musu kai.

  8. MDD na son a dauki matakin magance nutsewar ƴan ci-rani

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi kira da a ɗauki matakan da za su hana `yan ci-rani nutsewa a cikin teku.

    Mutane sama da saba`in ne suka rasu saboda kifewar da kwale-kwalen ya yi sakamakon lodin da ya wuce kima.

    Jami`an tsaron gaɓar tekun sun bayyana yadda suka yi ƙoƙari taimaka wa kwale-kwalen amma masu sukar ra`ayi sun zarge su da ɓata lokaci kafin kai agajin.

    Rahotanni sun ce abin da ya faru ranar Laraba, ya nuna buƙatar gudanar da bincike kan masu safarar mutane don tabbatar da ganin an gurfanar da su gaban shari'a.

    Wata sanarwa da hukumomin Majalisar Ɗinkin Duniya suka fitar ta bayyana buƙatar ƙasashen gaɓar teku, su samar da tashoshi don mutanen da suke zuwa ƙasashen ta cikin teku.

  9. Tattalin arzikin Ghana na nuna alamun daidaituwa - IMF

    Asusun bayar da lamuni na duniya IMF ya ce alamu na nuna cewa tattalin arzikin Ghana na samun daidato.

    IMF ya ce asusun ajiyar kuɗin ƙasashen wajen Ghana ya ƙaru, sannan darajar kuɗin ƙasar ya fara farfaɗowa, haka kuma an samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki.

    Tawagar IMF na kai ziyara akai-akai don tattaunawa da hukumomin Ghana kan ci gaban tattalin arzikin da aka samu a baya-bayan nan da kuma aiwatar da shirin ceto dala biliyan 3.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar, tawagar ma’aikatan IMF karkashin jagorancin Stéphane Roudet ta bukaci gwamnati da ta gaggauta yin garambawul a fasalin basussukan ƙasar domin ƙara amfana game da shirin.

    A halin yanzu Ghana na ƙoƙarin sake fasalin basussukan da ke waje da ya kai dala biliyan 20 daga cikin kusan dala biliyan 30 da ake binta.

    A watan mayun da ya gabata ne dai Ghana ta samu rancen IMF na tsawon shekaru 3 yayin da ƙasar ke ƙokarin fita daga matsalar tattalin arziki mafi muni cikin ƙarni da ya kai kashi 42.2% na hauhawar farashin kayayyaki.

  10. Jami'an tsaron Afrika ta kudu sun maƙale cikin jirgin sama a Poland

    Jami'an tsaron shugaban Afirka ta Kudu sun makale cikin wani jirgin sama a Poland na tsawon sa'o'i yayin da hukumomin ƙasar suka ƙi ba su dama su sauka a ƙasar.

    Jami'an tsaron na kan hanyarsu ta zuwa Ukraine inda Cyril Ramaphosa ke jagorantar tawagar zaman lafiya ta shugabannin ƙasashen Afirka.

    Rahotanni sun ce jirgin mai ɗauke da mutane sama da 120 ya sauka a filin jirgin sama na Chopin a Warsaw da sanyin safiyar ranar Alhamis.

    Jagoran jami'an tsaron da ke kula Mista Ramaphosa, Manjo Janar Wally Rhoode, ya ce gwamnatin Poland na yi wa tsaron shugaban ƙasar zagon ƙasa ta hanyar hana su sauka daga jirgin.

    "Sun janyo mana jinkiri marar dalili, sun ƙokarin jefa rayuwar shugaban kasarmu cikin hatsari", kamar yadda ya shaida wa manema labarai.

    "Saboda ya kamata a ce muna Kyiv a yanzu amma kuma ga abin da ya faru. Ina so ku ga yadda suke nuna wariyar launin fata."

    Hukumomin Poland ba su ce komai ba game da matakin wanda ka iya zama rikicin diflomasiya tsakanin ƙasashen biyu.

    Duk da abin da ya faru bai hana Mista Ramaphosa isa birnin Kyiv a jirgin ƙasa ba.

    Fadar shugaban Afirkar ta Kudu ta ce jakadan Afirka ta Kudu a Ukraine da kuma wakilin Ukraine na musamman a yankin Gabas ta Tsakiya da Afirka sun tarbi Mista Ramaphosa a lokacin da ya isa birnin Kyiv.

    Ana gaba ne kuma zai tafi ƙasar Rasha a wani yunƙurin da kasashen Afirka ke yi na ganin an kawo karshen rikicin ƙasashen biyu.

  11. Wani mutum ya mayar da littafin da ya ara bayan shekara 65

    Wani mutum ya mayar da wani littafin almara game da wata ƙasar kwatance mai taken George Orwell's 1984, zuwa ɗakin karatun Amurka da ke jihar Oregon bayan shekara 65.

    A wani saƙo da ya rubuta kuma ya cusa a cikin littafin, mutumin mai shekara 86 wanda ya bayyana sunansa da WP kawai ya ce kamata ya yi ya mayar da littafin zuwa ɗakin karatu na Mulnomah da ke Portland saboda fa'idar da yake shi har a zamanin yau.

    "Bayan sake-karantawa karo da dama, na fahimci cewa, fiye da kowanne lokaci a baya, kamata ya yi a sake buga wannan littafi don samun sa a cikin jama'a," rubutun ya ce.

    Labarin almarar ya yi nuni ne da taken da ya shafi mulkin kama-karya da kuma tsage gaskiya.

    "Ya kamata na mayar da wannan littafi ne a 1958, lokacin da nake shirin kammala karatu a [Jami'ar Jiha ta Portland], amma ban samu damar yin hakan ba," ya rubuta a cikin saƙon.

    "A yi min afuwa kan wannan dogon jinkiri. A shekara 86, ina so a ƙarshe na cire tunanin daga zuciyata," in ji shi.

    Mutumin ya ce a duk lokacin da ya sake karanta wani ɓangare na littafi, sai ya ji ya sake motsa masa kwaɗayin ya mayar da shi ɗakin karatun da ya ara.

    "Muhimman sassan littafin har yanzu suna da tasiri kamar yadda suke da shi shekara 65 da ta wuce," a cewarsa, inda takanas ya nunar da wani sashe a cikin shafi na 207. "A taƙaice ku ƙara kalmomin intanet da shafukan sada zumunta, za ku ji tamkar kuna karanta wani game da shekara ta 2023," ya ce.

    Littafin almarar wanda aka wallafa a 1949, an tsara shi ne a wata duniya inda gwamnatin kama-karya take murƙushe tunanin tsage gaskiya.

    Kasuwar littafin ta buɗe a Amurka cikin 2017 jim kaɗan bayan wani babban mai ba da shawara ga Donald Trump, wanda shi ne shugaban ƙasa a lokacin, ya ce fadar White House na fitar da "bayanai masu shigen gaskiya" a wani rikici game da girman taron mutanen da suka halarci bikin rantsar da shi.

    Da yake mayar da martani ga littafin da aka mayar, Ɗakin Karatu na Multnomah County ya ce ba za a ci mutumin tara a kan mayarwar a makare ba.

  12. Matan Indiya da ke faɗa da kafa matatar man Saudiyya

  13. Rasha ta yi garkuwa da ƙananan yara 150 - Ukraine

    Kasar Ukraine ta zargi Rasha da sace ƙananan yara 150 daga yankin Luhansk da Rasha ta mamaye, a gabashin ƙasar.

    A cewar Cibiyar Dakaru Masu Nuna Turjiya ga Mamayan Rasha a Ukraine, an kwashe yaran daga gundumar Starobilsk ta Luhansk a ranar 8 ga watan Yuni kuma aka kai su cibiyoyi biyu a yankin Karachay-Cherkess na Rasha.

    Cibiyar ta fitar da rahoton cewa, ana tilasta wa wasu yara a yankunan da aka mamaye a Ukraine yin gwajin cuta, domin kai su Rasha da niyyar yi musu magani.

    Jami'an Ukraine sun ce an kwashe fiye da yara 19,000 daga yankunan da aka mamaye tun lokacin da aka fara kai farmakin a watan Fabrairun 2022.

    A farkon wannan shekarar ne kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta bayar da sammacin kamo shugaba Putin na Rasha, bisa zarginsa da aikata laifukan yaƙi kan korar kananan yara daga Ukraine zuwa Rasha ba bisa ƙa'ida ba.

    Zarge-zargen da Rashar ta sha musantawa.

  14. Yaya canjin naira ya kaya a kasuwa bayan dunƙule harkar canji?

    Darajar naira ta faɗi a kasuwar harkokin zuba jari da fitar da kayayyaki ta Najeriya, inda aka canzar da dala ɗaya a kan N702.19 ranar Alhamis, a cewar kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN..

    Darajar naira ta ragu da kashi 5.75% idan aka kwatanta da yadda aka canzar da dala ɗaya a kan N664.04 ranar Laraba.

    NAN Ya ba da rahoton cewa, an buɗe kasuwar hada-hadar canjin kuɗin a N658.50 kan duk dala ɗaya a ranar Alhamis.

    Sai dai dala ɗaya ta kai ƙololuwar farashin N791 yayin hada-hadar ranar Alhamis, kafin ta daidaita a N702.19.

    Haka zalika yayin ciniki a ranar Alhamis a wata gaɓa, darajar naira ta tashi inda aka sayar da dala ɗaya a kan naira 461.

    An sayar da jimilar dala miliyan 70.72 a kasuwar harkokin zuba jari da fitar da kaya ta hukuma a ranar Alhamis.

  15. 'Maniyyatan Kano 156 ba za su je aikin hajjin bana ba'

    Hukumar jin Daɗin Alhazai ta jihar Kano ta ce akalla maniyyatan jihar 156 ne za su rasa aikin hajjin bana.

    Hakan ya faru ne sakamakon sayar da kujeru fiye da yadda aka ƙayyade da tsoffin jami’an hukumar da gwamnatin jihar ta dakatar suka yi.

    A lokacin da yake zantawa da manema labarai, Darakta Janar na hukumar, Laminu Rabiu ya ce hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta ware wa Kano kujeru 6,144, amma jami’anta sun sayar da ƙarin kujeru 156.

    Ya bayyana cewa za a binciki jami’an da suka aikata wannan laifi tare da gurfanar da su a gaban kotu, bayan kammala aikin Hajji bana.

    Daraktan ya kuma yin kira ga waɗanda abin ya shafa da su yi haƙuri, tare da alƙawarta musu cewa za a sanya su a cikin sahun farko a aikin Hajji mai zuwa.

    Ya zuwa yanzu Hukumar jin Daɗin Alhazan ta Kano, ta yi jigilar maniyyata 2,558, zuwa ƙasa mai tsarki.

  16. NEC ta ba da shawarar ɓullo da bai wa ma'aikata da marasa galihu tallafi

    Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya (NEC) ta ba da shawarar a bayar da tallafi ga ma’aikata da marasa a asar galihu don rage raɗaɗin da cire tallafin mai zai haifar a ƙasar.

    Gwamnan jihar Bala Mohammed ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Alhamis jin kaɗan bayan bayan kammala taron ƙaddamar da majalisar wadda mataimakin shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ke jagoranta ke jagoranta.

    Majalisar ta bayar da shawarar ne bayan da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya umarce ta da ɓullo da hanyoyin rage raɗadin.

    Gwamnan ya ce majalisar ta yi la’akari da shawarwarin da Hukumar Kula da Albashi da Ma’aikata ta Kasa ta bayar na biyan Naira biliyan 702 a matsayin alawus-alawus na rayuwa ga ma’aikatan gwamnati a wani ɓangare na rage raɗadin.

    A lokacin taron majalisar, an kafa wani kwamiti da zai gudanar da aiki, cikin makonni biyu, don yin nazarin hanyoyin da za a bi wajen raba kayan agajin.

  17. Ba makiyaya muka kashe a hari ta sama a Nasarawa ba - NAF

    Rundunar sojin saman Najeriya ta ce mutum 38 da ta kashe a lokacin wani hari ta sama cikin watan Janairu a garin Rukubi da ke ƙaramar hukumar Doma a jihar Nasarawa 'yan ta'addana ne ba 'makiyaya' ba kamar yadda ake zargi.

    Mai magana da yawun rundunar Air Commodore Ayodele Famuyiwa, ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja babban birnin ƙasar jim kaɗan bayan taron manema labarai da rundunar ke gudanarwar duk bayan mako biyu a shalkwatar hukumar tsaron ƙasar.

    Mista Famuyiwa ya ce 'yan ta'adda ne dakarun sojin saman suka kashe, kuma rundunar ta ƙaddamar da harin ne bayan da suka samu bayanan sirri kan ayyukan 'yan ta'addan.

    A cinin watan Janairu ne aka ƙaddamar da harin tare da kashe mutanen a garin Rukubi a lokacin da suke komawa jihar daga makwabciyarta Benue.

    A makon da ya gabata ne ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Humar Right Watch ta fitar da wani rahoto da a ciki ta zargi rundunar sojin saman Najeriyar da rashin bayar da cikakken bayani kan harin.

    Human Rights Watch ta ce ta yi nazari tare da tantance wasu hotuna guda takwas da ke nuna wasu gawarwakin, sannan a ranar 14 ga watan Maris ta ziyarci wani kabari da aka binne gawarwaki 31.

    A ranar 3 ga watan Mayu ne kungiyar kare hakkin bil adama ta Human Rights Watch ta rubuta wa babban hafsan hafsoshin sojin sama na Najeriya, wanda ke kula da rundunar sojin sama da ke gudanar da ayyukan soji, da kuma babban hafsan tsaron da ke kula da dukkan rundunonin soji ciki har da na sojojin sama, domin su bayar da cikakkun bayanai.

    Kungiyar ta kuma bayyana jinkirin da rundunar sojin saman ke yi a matsayin abin da ba a lamunta ba, inda ta buƙaci a gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa kan lamarin.

    Haka kuma HRW ta buƙaci rundunar sojin saman ta biya diyya ga iyalan waɗanda suka mutu a lokacin harin.

    Ita ma ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) mai kare muradun makiyaya a ƙasar ta zargi sojojin da kisan makiyayan da ba su ba kuma ba su gani a a lokacin hari.

    To sai dai Mista Famuyiwa ya kalubalanci ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da duk masu ikirarin cewa an kashe makiyaya a da shanu a lokacin harin da su bayyana wa duniya hujjarsu domin tabbatar da ikirarin.

  18. Assalamu alaikum

    Masu bin wannan shafin barkan mu da safiyar wannan rana ta Juma'a.

    Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a faɗin duniya, za mu fi mayar da hankali kan Najeriya da makwabtanta.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.